Maza-maza, Shalkwatar tsaro ta aika karin soji wani Yanki da Boko Haram kewa qawanya irin ta Metele

Rundunar sojin Najeriya ta sake tura dakarunta cike da kayan aiki domin su kare Jakana, wani gari a karamar hukumar Konduga da ke jihar Borno.
An gano rundunar wanda aka jona da na Operation Lafiya Dole a ranar Laraba, 5 ga watan Disamba cike da kayayyaki da dabarun yaki a Mainok, wani gari yan mil kadan daga Jakana.
Channels TV ta ruwaito cewa jami’an tsaro sun yada zango kusa da wuraren binciken ababen hawa a yankin inda ake ta bincikar matafiya sosai.

Hakan baya iya rasa nasaba da wani rahoto da ke yawo tun a ranar Talata na hare-hare da ake kaiwa kauyukan da ke kewaye da Jakana.

Wani dan jarida Ahmed Salkida ya wallafa a shafin twitter cewa “yan ta’addan Boko Haram sun fara taruwa a kauyen Mattari a karamar hukumar Konduga.
“Wajen na kusa da Jakana ko Benishek, akwai hukumomin sojin Najeriya a yankunan biyu, wasu majiyoyi suka ruwaito hakan.”
Sai dai rundunar sojin bata yi martani akan hakan ba tukuna.


Published on: December 6, 2018. at: 4:22 pm

Be the first to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published.


*